Siyasar Zamani

Siyasar Zamani Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Siyasar Zamani, Shopping & retail, No Karadua Street Barnawa, Kaduna.

Hoton barnar da mak**ai masu linzami na Iran s**a yi a yankunan da Isra'ila ta mamaye.Iran ta ƙaddamar da wani sabon shi...
19/03/2026

Hoton barnar da mak**ai masu linzami na Iran s**a yi a yankunan da Isra'ila ta mamaye.

Iran ta ƙaddamar da wani sabon shiri mai suna Wave 64 na Operation True Promise, wanda ke auna muhimman wurare na soji a yankunan da Isra'ila ta mamaye, ciki har da Filin Jirgin Sama na Ben Gurion, da wuraren samar da mai, da kuma sansanonin soji masu mahimmanci a Haifa da Rishon LeZion.

Wannan farmakin, wanda ya fara da asubahin ranar Alhamis, anyi amfani da na'urorin mak**ai masu linzami na zamani, ciki har da Qadr, Emad, Kheibar Shekan, da Khorramshahr, inda s**a kai hari kan duk wani abu da aka nufa.

Rundunar sojin ruwan Amurka ta biyar, wacce ke aiki a Tekun Fasha ita ma an kuma kai mata hari da mak**ai masu linzami masu matsakaicin zango. Majiyoyin Iran sun tabbatar da cewa ana ci gaba da aikin cikin nasara.

Sak**akon ayyukan, an ce sama da mazauna yankunan da aka mamaye miliyan 5 ne aka killace su a wuraren mafaka. Hukumomin Iran sun bayyana aikin a matsayin ramuwar gayya kai tsaye ga harin Isra'ila da Amurka.

Labarin Alhamis, 19 Maris 2026 1:49 PM. Daga Presstv.ir ✍️

Siyasar Zamani

19/03/2026

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana da Firaministan Burtaniya Keir Starmer a wani ɓangare na ziyarar kwanaki biyu da yake yi a Landan.

Sun haɗu ne a gidan gwamnatin Burtaniya na 10 Downing Street da ke tsakiyar birnin Landan a ranar Alhamis.

Siyasar Zamani

Wani ɗan jarida na Amurka ya tayar da kura a yanar gizo bayan da ya wallafa cewa Netanyahu ya mutuWani ɗan jarida dan ƙa...
19/03/2026

Wani ɗan jarida na Amurka ya tayar da kura a yanar gizo bayan da ya wallafa cewa Netanyahu ya mutu

Wani ɗan jarida dan ƙasar Amurka mai suna Ethan Levins ya jawo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta bayan da ya yi iƙirarin cewa Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya mutu tun ranar 8 ga watan Maris.

Levins ya yi zargin cewa ɗan Netanyahu, Yair Netanyahu, bai wallafa komai a dandalin X (Twitter) na tsawon kwanaki bakwai ba, yana danganta hakan da al’adar Yahudawa ta “shiva”, wato lokacin makoki bayan rasuwar ɗan uwa.

Sai dai rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na yamma sun nuna cewa mutuwar Netanyahu ba gaskiya bane, duk da an kalubalanci ya fito ya bayyana muddin yana raye.

Duk da cewa ofishin Firaministan Isra’ila ya karyata wadannan rahotanni, yana mai cewa labaran ƙarya ne marasa tushe, amma an zarge su da wallafa hotuna da bidiyoyi kirkirarru daga AI don kawar da hankalin mutane.

Isra'ila ta nuna cewa wasu daga cikin masu cewa Netanyahu ya mutu sun samo asali ne daga kafafen yaɗa labarai masu alaƙa da Iran, waɗanda s**a yada bayanai ba tare da hujja ba, abin da masana ke gani a matsayin wani ɓangare na yaƙin bayanai (information warfare).

Haka kuma, bidiyoyi da Isra'ila ke yadawa a yanar gizo suna cigaba da haifar da ƙarin rudani, inda wasu s**a cigaba da zargin cewa hotunan Netanyahu na iya zama na fasahar “deepfake”, lamarin da ya ƙara rikitar da jama’a a wannan zamani na fasahar zamani.

Siyasar Zamani

Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda 61 a Malam Fatori da ke arewa maso gabashin ƙasar nan.Rahotanni sun ce lamarin ya...
18/03/2026

Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda 61 a Malam Fatori da ke arewa maso gabashin ƙasar nan.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da 'yan'taddan s**a yi ƙoƙarin shige sansanin sojin da ke garin Malam Fatori a jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya

Rahotanni na cewa sojin ƙasa da na saman Nijeriya sun yi nasarar kashe ‘yanta’adda aƙalla 61 a garin Malam Fatori da ke jihar Borno a arewa maso gabas.

Wani rahoton da Zagazola Mak**a ya fitar wanda babban mai bai wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan dabaru da watsa labarai, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafinsa na X, ya ce lamarin ya auku ne a lokacin ‘yanta’addan s**a nemi kutsawa cikin sansanin soji a Malam Fatori da ke ƙaramar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Rahoton ya ambato majiyoyin tsaro suna cewa ‘yanta’addan sun ƙaddamar da harin da sanyin safiyar Laraba ne inda s**a nufi sansanin sojin da ƙafa kuma s**a yi amfani da jirage mara matuƙa a wani yunƙuri na karya katangar sansanin sojin da ƙarfin hali.

Sai dai martani mai ƙarfi na haɗin gwiwa da dakarun ƙasa da na sama s**a yi ya fi ƙarfin ‘yanta’addan.

Kazalika wata sanarwar da daraktan hulɗa da jama’a da watsa labarai na rundunar sojin saman Nijeriya, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar kuma Usman Kuka Sheka tsohon kakakin sojin Nijeriya ya wallafa a shafinsa na Fabeook, ta tabbatar da aikin da sojin saman ta yi a Malam Fatori.

“Aikin na haɗin gwiwa ya yi nasarar hana masu tayar da ƙayar bayan karya katangun tsaro, lamarin da ya ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi na daidaita lammura a garuruwan da ke kan iyakoki,“ in ji sanarwar.

Siyasar Zamani

RAHOTO....Ma’aikatar Leken Asiri ta Iran ta bayyana yadda ta yi nasarar murkushe wasu manyan ayyukan ‘yan leƙen asiri da...
18/03/2026

RAHOTO....

Ma’aikatar Leken Asiri ta Iran ta bayyana yadda ta yi nasarar murkushe wasu manyan ayyukan ‘yan leƙen asiri da masu cin amanar ƙasa da ke da alaƙa da Izra@ila, waɗanda s**a yi ƙoƙarin anfani da yanayin yaƙi a cikin ƙasar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Laraba, ma’aikatar ta ce bayan sa ido mai tsauri kan mutanen da ake zargi da yi wa Isra’ila aiki tare da taimakawa shirye-shiryen adawa da Iran, an k**a akalla mutane daei da sha daya (111) masu cin amanar ƙasa da ke cikin ƙungiyoyin masu goyon bayan sarauta a wasu hare-haren rigakafi da aka kai a jihohi 26 na ƙasar.

Sanarwar ta bayyana waɗannan a matsayin “makiyan Iran masu alaka da Izra@ila ”, inda aka ce suna ƙoƙarin tada tarzoma a cikin ƙasar. Haka kuma an ƙwace mak**ai da dama ciki har da bindigogi, wuƙaƙe, sanduna, na’urorin lantarki masu girgiza jiki, feshi, tutoci na bogi da sauransu.

Jami’an leƙen asiri tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro sun kuma gano tare da k**a wasu ‘yan leƙen asiri guda huɗu da ke aiki ga Amurka da abokan haɗin gwiwarta, ciki har da mutum biyu a lardin Hamadan.

An bayyana cewa waɗannan ‘yan leƙen asirin sun samu horo na musamman a ƙarƙashin wata cibiyar al’adun Amurka a wata ƙasa makwabciya, inda s**a rika tura bayanai kan wuraren ajiyar mak**an sojojin Iran zuwa ga abokan gaba na Amurka da Isra’ila.

Haka kuma an k**a wasu biyu a lardin West Azarbaijan, waɗanda ke aiki da wata cibiyar leƙen asiri da ke yankin Kurdistan na Iraq.

Ma’aikatar ta ƙara da cewa an k**a wasu manyan kayan mak**ai guda biyu, ciki har da bindigogi 29, bindigogin AK-47 guda biyu tare da harsasai masu yawa, yayin da ake ƙoƙarin shigo da su daga Kurdistan na Iraq zuwa lardin Kermanshah.

A wani samame daban, an ƙwace wasu mak**ai a lardin Khorasan Razavi, ciki har da bindigogi guda 8, harsasai 161, na’urar sadarwa ta rediyo da kuma kwalaben wuta (Molotov cocktails) guda 21, tare da k**a wasu mutane da dama.

Bugu da ƙari, mutane 21 sun shiga hannu a jihohin Tehran, Hamadan, Fars da West Azarbaijan bisa zargin aikawa da hotuna, bidiyo da bayanai masu muhimmanci ga tashar talabijin ta “Iran International” da ake dangantawa da Izra@ila.

Haka kuma jami’an tsaro sun gano tare da k**a manyan na’urorin sadarwa na tauraron dan adam guda 350 (Starlink), waɗanda ake ƙoƙarin shigo da su ba bisa ƙa’ida ba daga wasu ƙasashen Larabawa na Tekun Fasha zuwa lardin Hormozgan.

Siyasar Zamani

Gwamnatin Kano za ta faɗi matsayarta kan hawan Sallah a yauGwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa za ta sanar da matsayart...
18/03/2026

Gwamnatin Kano za ta faɗi matsayarta kan hawan Sallah a yau

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa za ta sanar da matsayarta kan hawan Sallah a jihar.

Mai magana da yawun Gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana hakan a wani bayani da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

"Gwamnatin Kano za ta fadi matsayar ta kan hawan sallah nan da yan awannan kadan ta bakin Kwamashinan Yada Labarai.

"A jira cikin lumana..."

Bayanin nasa na zuwa ne a yayin da ake takaddama kan wanda zai jagoranci hawan Sallah tsakanin Sarkin Kano Muhammad Sanusi II da Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero.

Siyasar Zamani

Wannan mutumin na jikin hoton nan, yana daga cikin dalilan da yasa Izra@ila take samun bayanai akan motsin shugabannin I...
18/03/2026

Wannan mutumin na jikin hoton nan, yana daga cikin dalilan da yasa Izra@ila take samun bayanai akan motsin shugabannin Iran har suke kai musu hari suna shahadantar dasu, Izra@ila tana da yan leken asiri masu yawa a cikin kasar Iran wadanda suke aikewa da bayanan sirri...

Iran kasa ce dake da yawan mutane har kusan miliyan dari domin sun haura miliyan chasa'in kunga kenan dole a samu wadanda raayinsu baizo daya da raayin jagororin addini na Iran ba...

Jami’an tsaron Iran suna kokari sosai wajen lalubo yan leken asirin Izra@ila dake cikin kasar Iran...

Yau din nan aka SHEKE wannan tsinannen bayan samunsa da hannu wajen aikewa da rahotanni zuwa Izra@ila akan sensitive information da s**a shafi shugabanni da kasar Iran...

Muna adduar Allah ya cigaba da tona asirin yan leken asiri da suke baiwa Izra@ila bayanai daga cikin kasar Iran...

Siyasar Zamani

Malam Abdulaziz Abdulaziz Ya Raba Tallafin Shinkafar Azumi Ga Mutum Sama Da Dubu 30Daga. Ibrahim Imam Ikara   Babban Mat...
18/03/2026

Malam Abdulaziz Abdulaziz Ya Raba Tallafin Shinkafar Azumi Ga Mutum Sama Da Dubu 30

Daga. Ibrahim Imam Ikara

Babban Mataimaki Na Musamman Ga Shugaban Ƙasa Kan Yaɗa Labarai, Malam Abdulaziz Abdulaziz ya raba tallafin shinkafar azumi ga sama da mutum 30,000 a Arewacin Najeriya, k**ar yadda ya saba a duk lokacin watan Ramadhan.

An raba shinkafar ne ta hannun ƙungiyoyi masu zaman kan su, da ƙungiyoyin jin ƙai, da kuma ƙungiyoyin siyasa.

A wani rubutu da Chairman, Alhaji Bashir Abdullahi El-bash, ya wallafa a shafukan yaɗa zumunta ya bayyana yadda matasa 200 su ka amfana da shinkafa 50kg ta hannun sa daga Malam Abdulaziz Abdulaziz.

Haƙiƙa irin wannan aiki na Malam Abdulaziz Abdulaziz ya na sanya farin ciki a zukatan al'umma, tare da ƙarfafa zumunci da haɗin kai a tsakanin shugabanni da waɗanda a ke jagoranta.

Ko da mutum ya na da ƙarfin da ya ke da Shinkafar, a tuna da shi a ba shi kyauta wata alama ce ta mutunci da daraja, da karamci.

Mu na miƙa godiya da jinjina, tare da yabawa na ayyukan alheri da Malam Abdulaziz Abdulaziz ya ke yi, Allah ya saka da mafificin alheri, Allah ya ƙara ɗaukaka, Allah ya sa a ci gaba da irin wannan hidima ga al'umma.

Siyasar Zamani

18/03/2026
18/03/2026

Allah ya taimaki sojojin Nijeriya ✊

Siyasar Zamani

Iran Ta Rufarwa Tel Aviv Da Ruwan Mak**ai Masu Linzami A Wani Harin Fansa a Daren LarabaA daren jiya Laraba, 18 ga watan...
18/03/2026

Iran Ta Rufarwa Tel Aviv Da Ruwan Mak**ai Masu Linzami A Wani Harin Fansa a Daren Laraba

A daren jiya Laraba, 18 ga watan Maris, 2026, fargaba da tashin hankali sun mamaye birnin Tel Aviv na ƙasar Isra'ila, bayan da dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran (IRGC) s**a harba jerin mak**ai masu linzami samfurin Khorramshahr-4 da Qadr zuwa tsakiyar birnin.

Wannan hari, wanda aka bayyana a matsayin daya daga cikin mafi muni tun bayan barkewar rikicin kasashen biyu a kwanakin baya, ya raba mazauna birnin da barci, inda ƙararrakin fashe-fashe da sirens s**a karade sararin samaniya.

Rahotannin farko daga hukumomin lafiya na Magen David Adom sun tabbatar da mutuwar wasu mutane guda biyu, a yankin Ramat Gan. An bayyana cewa makamin ya afka wa gidansu ne kafin su samu damar shiga ramin kariya (bunker).

Baya ga asarar rayuka, harin ya haddasa:
• Gobara: Mak**an sun haddasa gobara a wurare daban-daban, ciki har da unguwar Holon inda wutar lantarki ta yanke sak**akon lalacewar igiyoyin wuta.

• Tashar Jirgin Kasa: An dakatar da zirga-zirgar jiragen ƙasa bayan barbashin mak**an ya lalata sassa na tashar Savidor Center da ke Tel Aviv.

• Na'urar Iron Dome: Rahotanni sun nuna cewa tsarin kariya na Isra'ila ya fuskanci kalubale wajen tunkarar sabbin mak**an Iran masu dauke da fasahar rarrabuwa (cluster warheads), wadanda ke da wahalar kakkabowa.

Dalilin Harin Ramuwar Gayya

Iran ta fito fili ta bayyana cewa wannan hari martani ne ga kisan babban jami'in tsaron kasar, Ali Larijani, da kuma kwamandan dakarun Basij, Gholamreza Soleimani, wadanda Isra'ila ta kashe a ranar Litinin yayin wani harin bam a Tehran.

Ali Larijani shi ne sakataren majalisar tsaro ta kasar Iran, kuma ana daukarsa a matsayin daya daga cikin manyan ginshikan gwamnatin Tehran.

Halin Da Ake Ciki Yanzu

A halin yanzu, jami'an ceto suna ci gaba da kwashe baraguzan gine-gine da kuma duba adadin mutanen da s**a jikkata, yayin da ake fargabar cewa adadin wadanda s**a mutu na iya karuwa. Firayim Ministan Isra'ila ya kira taron gaggawa na majalisar tsaro don tattauna mataki na gaba, yayin da Amurka ta yi kira da a kwantar da tarzoma don gudun kada yankin Gabas Ta Tsakiya ya tsandama cikin gagarumin yaki.

Siyasar Zamani

Address

No Karadua Street Barnawa
Kaduna

Telephone

+2348131693821

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Siyasar Zamani posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share