06/07/2017
LOKUTA GUDA-(5) BIYAR DA AKE BUDE KOKOFIN
SAMA.
1-Kafin Sallar Azzuhur.
Manzon Allah s.a.w yana cewa:
(Lallai ana bude kokofin sama lokacin da rana
tayi zawali ba'a kullesu har sai anyi Sallar
azzuhur, shi yasa nake so aiyukan alkhairi nawa
ahau sama dasu a wannan lokacin).
@ ﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ
ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ - ﺭﻗﻢ: ( 1532 )
NB
"Shi yasanya Annabi s.a.w ya sunnan ta mana
yin nafila raka'a hudu a awannan lokacin kamar
yadda yazo a cikin"
2-Lokacin kowane kiran sallah.
Manzon Allah s.a.w yace:
(Idan kayi kiran Sallah ana bude kokofin
sama,kuma sai a amshi adduar wanda yayi
addua a wannan lokacin).
@ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ - ﺭﻗﻢ : ( 260) ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ -
ﺭﻗﻢ : ( 818 ).
NB
"Dan haka mu yawaita rokon Allah bayan kiran
sallah lokacine na amsa addua kamar yadda
Annabi s.a.w yace".
3-Lokacin jiran sallah a masallaci bayan an gama
wata sallah,kamar tsakanin magariba da Isha'i
ko tsakanin La'asar zuwa Magariba.
Manzon Allah s.a.w yana cewa:
(Kuyi albishir,wannan Ubangijinku ne ya bude
wata kofa daga cikin kokofin sama,yana alfahari
da ku a wajan mala'ikunsa yana cewa:ku kulli
bayina sun gabatar da farilla dana dora masu
kuma amma suna jiran wata sallar).
@ ﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ - ﺭﻗﻢ: ( 445) ﺻﺤﻴﺢ
ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ - ﺭﻗﻢ : (36 )
NB
"Wanda ya zauna a wajan sallarsa yana jiran
wata sallah mala'iku sunayi masa addua kuma
ana rubuta masa ladar yana cikin sallah sannan
ana bude masa kofar sama dan amsa
adduarsa".
4-Idan dare yayi Rabi Manzon Allah s.a.w yana
cewa:
(Idan dare yayi rabi ana bude kokofin sama,sai
wani mai kira yayi kira yace: Shin akwai mai
rokon Allah a amsa masa?akwai mai roko
abashi?akwai mai da damuwa a yaye masa?
babu wani musulmi da zai roki Allah a wannan
lokaci face Allah ya amsa masa,sai dai
mazinaciyar da take amfanuwa da zinar ko
kudin zina....).
@ ﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ - ﺭﻗﻢ : ( 786)
ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ - ﺭﻗﻢ: ( 2971 )
5-Lokacin yin addua da wadan nan kalmomi:
[ * ﺍﻟﻠﻪُ ﺃﻛﺒﺮُ ﻛﺒﻴﺮًﺍ ﻭﺍﻟﺤﻤﺪُ ﻟﻠﻪ ﻛﺜﻴﺮًﺍ ﻭﺳﺒﺤﺎﻥ ﺍﻟﻠﻪِ ﺑﻜﺮﺓً ﻭﺃﺻﻴﻞً*ﺍ ]
[*ALLAHU AKBAR KABIRAN WALHAMDU LILLAHI
KATHIRAN WA SUBHANALLAH BUKRATAN WA
ASILA*]
Daya daga cikin sahabban Manzon s.a.w yana
cewa:
"Wani lokaci muna sallah tare da Manzon Allah
s.a.w sai wani mutum daga cikin mutane yace:
[ * ﺍﻟﻠﻪُ ﺃﻛﺒﺮُ ﻛﺒﻴﺮًﺍ ﻭﺍﻟﺤﻤﺪُ ﻟﻠﻪ ﻛﺜﻴﺮًﺍ ﻭﺳﺒﺤﺎﻥ ﺍﻟﻠﻪِ ﺑﻜﺮﺓً ﻭﺃﺻﻴﻞً*ﺍ ]
[*ALLAHU AKBAR KABIRAN WALHAMDU LILLAHI
KATHIRAN WA SUBHANALLAH BUKRATAN WA
ASILA*]sai Manzon Allah s.a.w yace:
(Wanene ya fadi wadan nan kalmomin??) Sai
wani mutum yace nine ya Manzon Allah. Sai
yace:
(An amsa adduarka kuma an bude maka kofofin
sama,saboda da wadan nan kalmami).
Ibn Umar R.A yake cewa:
"Ban taba barin fadar wadan nan kalmomin ba
lokacin addua tun daga lokacin da naji Manzon
S.a.w ya fadi haka".
@ ﺻﺤﻴﺢ ﻣﺴﻠﻢ (601 ).
Mu hada wannan muyi turawa yan uwan mu
domin amfanin juna duniya da lahira.
ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻤﺒﺎﺭﻙ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ :
Yana cewa:
"Ban san wata daraja mafi falala da daukaka
bayan Annabta kamar yada Ilimi mai amfani".
@ ﺗﻬﺬﻳﺐ ﺍﻟﻜﻤﺎﻝ ( ٢٠ /١٦ ).
Allah ya sanya mu cikin wadan da ake amsa
adduar su.